Loading surah...
Back to Hausa Quran
29 Ayahs • Meccan
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ
Mãsu gudu suna ɓũya.
وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
Page 1 of 2 (29 ayahs)