Loading...
Language: Hausa
آمَنَ الرَّسُولُ بِمَا أُنْزِلَ إِلَيْهِ مِن رَّبِّهِ وَالْمُؤْمِنُونَ ۚ كُلٌّ آمَنَ بِاللَّـهِ وَمَلَائِكَتِهِ وَكُتُبِهِ وَرُسُلِهِ لَا نُفَرِّقُ بَيْنَ أَحَدٍ مِّن رُّسُلِهِ ۚ وَقَالُوا سَمِعْنَا وَأَطَعْنَا ۖ غُفْرَانَكَ رَبَّنَا وَإِلَيْكَ الْمَصِيرُ ﴿٢٨٥﴾ لَا يُكَلِّفُ اللَّـهُ نَفْسًا إِلَّا وُسْعَهَا ۚ لَهَا مَا كَسَبَتْ وَعَلَيْهَا مَا اكْتَسَبَتْ ۗ رَبَّنَا لَا تُؤَاخِذْنَا إِن نَّسِينَا أَوْ أَخْطَأْنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تَحْمِلْ عَلَيْنَا إِصْرًا كَمَا حَمَلْتَهُ عَلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِنَا ۚ رَبَّنَا وَلَا تُحَمِّلْنَا مَا لَا طَاقَةَ لَنَا بِهِ ۖ وَاعْفُ عَنَّا وَاغْفِرْ لَنَا وَارْحَمْنَا ۚ أَنْتَ مَوْلَانَا فَانْصُرْنَا عَلَى الْقَوْمِ الْكَافِرِينَ ﴿٢٨٦﴾
(285) Aamanar-Rasoolu bimaa 'unzila ilayhi mir-Rabbihi wal mu'minoon, kullun 'aamana billaahi wa malaa'ikatihi wa Kutubihi wa Rusulih, laa nufarriqu bayna 'ahadim-mir-Rusulih, wa qaaloo sami'naa wa 'ata'naa ghufraanaka Rabbanaa wa 'ilaykal-maseer. (286) Laa yukallifullaahu nafsan 'illaa wus'ahaa, lahaa maa kasabat wa 'alayhaa mak-tasabat, Rabbanaa laa tu'aakhidhnaa 'in naseenaa 'aw 'akhta'naa, Rabbanaa wa laa ta'hmil 'alaynaa 'isran kamaa hamaltahu 'alal-ladheena min qablinaa, Rabbanaa wa laa tu'hammilnaa maa laa taaqata lanaa bihi, wa'fu 'annaa, waghfir lanaa war'hamnaa, 'Anta Mawlaanaa fansurnaa 'alal-qawmil-kaafireen
(285) Manzo ya yi imani da abin da aka saukar masa daga Ubangijinsa, da (haka nan) muminai. Dukanninsu sun yi imani da Allah da mala'ikunSa da littafanSa da manzonniSa, [suna cewa], "Ba ma rarrabewa tsakanin ɗaya daga cikin manzanninSa." Kuma suna cewa, "Mun ji kuma mun yi biyayya. [Muna neman] gafararKa, Ubangijinmu, kuma zuwa gare Ka ne makoma ta ƙarshe take. (286) Allah ba Ya ɗorawa rai sai abin da yake iyawarsa. Yana da [sakamakon] abin da ya samu na [alheri], kuma zai ɗauki [sakamakon] abin da ya aikata na [sharri]. "Ubangijinmu, kada Ka kama mu idan mun yi mantuwa ko mun yi kuskure. Ubangijinmu, kuma kada Ka ɗora nauyi a kanmu kamar yadda Ka ɗora shi a kan waɗanda suka gabace mu. Ubangijinmu, kuma kada Ka ɗora mana abin da ba mu da ikon ɗauka. Kuma Ka yafe mana; kuma Ka gafarta mana; kuma Ka yi mana rahama. Kai ne majibincinmu, saboda haka Ka ba mu nasara a kan mutanen da suke kafirai. (Sura Baqarah 2: 285-286)
Reference: Al-Bukhari, Fathul Bari 9/94, Muslim 1/554, Lamba 807