Loading...
Language: Hausa
Shahr bin Hawshab (R) ya ce: “Na ce wa Umm Salamah (RA): ‘Ya Uwar Muminai! wace addu'a ce Manzon Allah (ﷺ) ya fi yawan yi lokacin da yake tare da ke?” Ta ce: ‘Addu'ar da ya fi yawan yi ita ce -
يَا مُقَلِّبَ الْقُلُوبِ ثَبِّتْ قَلْبِيْ عَلَى دِيْنِكَ
Ya Muqallibal-qulubi, thabbit qalbi 'ala dinik
Ya Mai Juya Zukata! Ka tabbatar da zuciyata akan addininKa. Sai na ce: Ya Manzon Allah (ﷺ), me ya sa kake yawan yin addu'a haka. Ya ce: ‘Ya Umm Salamah! Lallai, babu wani dan adam face zuciyarsa tana tsakanin Yatsu Biyu na Yatsun Allah, don haka wanda Ya so Yana tabbatar da shi, kuma wanda Ya so Yana karkatar da shi.
Reference: Sahih (Albani). Tirmidhi: 3522