Loading...
Language: Hausa
An ruwaito daga Shaqiq (RA): Hudhaifa (RA) ya ga wani mutum wanda baya yin Ruku'u da Sujada yadda ya kamata. Sai ya ce masa, "Ba ka yi sallah ba kuma idan ka mutu to za ka mutu a kan addinin da ba na Muhammad (ﷺ) ba." Qatadah (RA) ya ce, Annabi (ﷺ) ya ce, mafi munin ɓarawo shine wanda yake sace sallah. Sahabbai suka ce, ta yaya ake sace sallah? Annabi (ﷺ) ya ce: Wanda baya cika Ruku'unsa da Sujadarsa.
Reference: [1] Bukhari: 791 [2] Sahih (Albani). Mishkat: 885