Loading...
Language: Hausa
An ruwaito Jabir Ibn Abdillah (RA): A wani wuri a cikin dogon hadisinsa na Hajjin Annabi (ﷺ), ya ce, 'Sannan Manzon Allah (ﷺ) ya kwanta har zuwa asuba. Bayan gari ya waye, ya yi sallar asuba da kiran sallah ɗaya da ikama ɗaya. Sannan ya zo Al-Mash'arul Haram a kan Qaswaa. A nan ya juya ga Alƙibla kuma ya yi addu'a ga Allah da bayyana fifikon Allah, mulkinSa da ɗaya kasancewarSa. Ya tsaya a nan har sai da hasken safe ya yi haske sosai. Sannan ya tafi kafin rana ta fito.' [2]
Reference: [1] Sunan abin hawan Annabi (ﷺ) [2] Muslim: 1218