Loading...
Language: Hausa
Abdullah bin Mas'ud (RA) ya ruwaito: "Manzon Allah (ﷺ) ya koya mana Tashahhud don Sallah da Tashahhud don Al-Hajah." Ya ce: "Tashahhud don Sallah shi ne:
إِنَّ الْحَمْدَ لِلَّهِ نَحْمَدُهُ وَنَسْتَعِينُهُ وَنَسْتَغْفِرُهُ وَنَعُوذُ بِاللَّهِ مِنْ شُرُورِ أَنْفُسِنَا وَمِنْ سَيِّئَاتِ أَعْمَالِنَا، مَنْ يَهْدِهِ اللَّهُ فَلَا مُضِلَّ لَهُ وَمَنْ يُضْلِلْ فَلَا هَادِيَ لَهُ أَشْهَدُ أَنْ لَّا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ حَقَّ تُقَاتِهِ وَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنْتُمْ مُّسْلِمُونَ يَا أَيُّهَا النَّاسُ اتَّقُوا رَبَّكُمُ الَّذِي خَلَقَكُمْ مِّن نَّفْسٍ وَاحِدَةٍ وَخَلَقَ مِنْهَا زَوْجَهَا وَبَثَّ مِنْهُمَا رِجَالًا كَثِيرًا وَنِسَاءً ۚ وَاتَّقُوا اللَّهَ الَّذِي تَسَاءَلُونَ بِهِ وَالْأَرْحَامَ ۚ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَلَيْكُمْ رَقِيبًا يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ وَقُولُوا قَوْلًۭا سَدِيدًا يُصْلِحْ لَكُمْ أَعْمَالَكُمْ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ذُنُوبَكُمْ وَمَنْ يُطِعِ اللَّهَ وَرَسُولَهُ فَقَدْ فَازَ فَوْزًا عَظِيمًا
Innal-hamda lillaah nahmaduhu wa nasta‛eenuhu wa nastaghfiruhu, wa na‛oodhu billaahi min shuroori anfusinaa wa min sayyi’aati a‛maalinaa, man yahdih-illaahu fa laa mudilla lah, wa man yudlil fa laa haadiya lah, ash-hadu an laa ilaaha ill-Allaahu, wa ash-hadu anna muhammadan ‛abduhu wa rasooluh Yaa ayyuhal-ladheena aamanut-taqullaaha ‘haqqa tuqaatihi walaa tamootunna illaa wa antum muslimoon yaa ayyuhan-naasut-taqoo rabbakum-ul-ladhee khalaqakum min nafsin wa’hidatin, wa khalaqa minhaa zawjahaa, wa bath-tha minhumaa rijaalan katheeran wanisaa’-an, wat-taqullaahal-ladhee tasaa’aloona bihi wal ar’haam, inn-Allaaha kaana ‛alaykum raqeebaa Yaa ayyuhal-ladheena aamanut-taqullaaha wa qooloo qawlan sadeeda, yusli’h lakum a‛maalakum wa yaghfir lakum dhunoobakum, wa man yuti‛illaaha wa rasoolahu faqad faaza fawz-an ‛azeemaa
Lallai dukkan Yabo na Allah ne, muna gode maSa, muna neman taimakonSa kuma muna neman gafararSa. Muna neman tsari da Allah daga sharrin rayukanmu da daga sharrin ayyukanmu. Wanda Allah Ya shiryar ba zai taɓa ɓacewa ba, kuma wanda Allah Ya ɓatar, babu mai iya shiryar da shi. Na shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma na shaida cewa Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa. (sannan ya karanta ayoyi masu zuwa) Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ji tsoron Allah yadda ya kamata a ji tsoronSa, kuma kada ku mutu sai kuna Musulmai; [1] Ya ku Mutane! Ku ji tsoron Ubangijinku, Wanda Ya halicce ku daga rai ɗaya, da daga gare shi Ya halicci matarsa, da daga gare su ya halicci maza da mata masu yawa, da ku ji tsoron Allah Wanda kuke roƙon juna da Shi (haƙƙoƙi). Lallai, Allah Mai Kula ne a kanku; [2] Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku ji tsoron Allah, da ku faɗi (koyaushe) gaskiya Zai shiryar da ku don aikata kyawawan ayyuka da zai gafarta muku zunubanku. Da wanda ya yi biyayya ga Allah da ManzonSa lallai ya samu rabauta mai girma. [3] Sannan zai yi magana game da bukatunsa. [4]
Reference: [1] Suratul Ali Imran: 3:102 [2] Suratul Nisa: 4:1 [3] Suratul Ahzab: 33:70-71 Sahih (Albani) Tirmidhi: 1105