Loading...
Language: Hausa
Abbas ɗan Abdul-Muttalib (RA) ya ce: "Na ce: 'Ya Manzon Allah (SAW), koya mini wani abu da zan roƙi Allah [Mai girma da Ɗaukaka].' Ya (SAW) ya ce: 'Roƙi Allah Al-Afiyah (Afuwa/Lafiya).' Sannan na tsaya na kwana ɗaya, sannan na zo na ce: 'Ya Manzon Allah (SAW), koya mini wani abu da zan roƙi Allah.' Sai ya (SAW) ya ce mini: "Ya Abbas, ya baffan Manzon Allah! Roƙi Allah Al-Afiyah (Afuwa/Lafiya) a duniya da Lahira."
Reference: Sahih (Albani). Tirmidhi: 3514