Loading...
Language: Hausa
Wani mutum ya zo wurin Manzon Allah (SAW), ya ji shi yana cewa: "Ya Manzon Allah (SAW), me zan ce idan zan roƙi Allah?" Ya (SAW) ya ce: "Ka ce:
اَللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي وَارْحَمْنِيْ وَعَافِنِيْ وَارْزُقْنِيْ
Allaahumma-ghfir li warhamni wa 'aafini warzuqni
Ya Allah, Ka gafarta mini, Ka yi mini rahama, Ka ba ni lafiya kuma Ka azurta ni. Kuma ya ware yatsunsa huɗu banda babban yatsa ya ce: "Waɗannan za su haɗa maka al'amuran addininka da na duniya."
Reference: Sahih. Ibn Majah: 3845