Loading...
Language: Hausa
Abin da ya faru shi ne kamar haka: Cewa Annabi (SAW) ya ba shi Dinari ɗaya don ya sayo masa tunkiya. Urwa ya sayo masa tumaki biyu da kuɗin. Sannan ya sayar da ɗaya daga cikin tumakin akan Dinari ɗaya, kuma ya kawo Dinari ɗaya da tunkiya ɗaya ga Annabi (SAW). A kan haka, Annabi (SAW) ya roƙi Allah ya sanya masa albarka a cikin cinikayyarsa. Don haka Urwa ya kasance yana samun riba (daga duk wata ciniki) koda ƙura ya siya.
Reference: Bukhari: 3642