Loading...
Language: Hausa
Da suka ji muryarsa, dariya ta ɗauke musu kuma suka ji tsoron la'anarsa. Sai Annabi (SAW) ya ce:
اَللَّهُمَّ عَلَيْكَ بِأَبِي جَهْلِ بْنِ هِشَامٍ وَعُتْبَةَ بْنِ رَبِيْعَةَ وَشَيْبَةَ بْنِ رَبِيْعَةَ وَالْوَلِيْدِ بْنِ عُقْبَةَ وَأُمَيَّةَ بْنِ خَلَفٍ وَعُقْبَةَ بْنِ أَبِيْ مُعَيْطٍ
Allaahumma ‘Alaika bi abi jahl ibn Hisham, wa Utbath ibn Rabi'ah, wa Shaibah ibn Rabi'ah, wal Walid ibn Uqbah, wa Umayyah ibn Khalaf, wa Uqbah ibn abi Mu'ait
Ya Allah, Ka isar mana ga Abu Jahl ɗan Hisham, da Utba ɗan Rabi'a, da Shaiba ɗan Rabi'a. Walid ɗan Uƙba, Umayya ɗan Khalaf, Uƙba ɗan Abi Mu'ait. Ibn Mas'ud (RA) ya ce, "Na rantse da Wanda ya aiko Muhammadu (SAW) da gaskiya, na ga (duk) wadanda ya ambata sume a kwance a Ranar Badar. An ja gawarwakinsu an jefa su cikin wani rami kusa da filin daga". A wata ruwayar, "Na rantse da Allah na gan su a kwance a filin daga na Badar. Kasancewar ranar akwai zafi, launin fatarsu ya canza (yana nuna alamar ruɓewa)."
Reference: Muslim: 1794