Loading...
Language: Hausa
Ubayy ɗan Ka'b (RA) ya ce: "Na ce: 'Ya Manzon Allah! Lallai ina yawan yi maka Salati. Kaso nawa na Salat ina ya kamata in yi maka?' Ya (SAW) ya ce: 'Yadda kake so.'" [Ya ce:] "Na ce: 'Rubu'i?' Ya (SAW) ya ce: 'Yadda kake so. Amma idan ka ƙara zai fi maka.' Na ce: 'To rabi?' Ya (SAW) ya ce: 'Yadda kake so. Kuma idan ka ƙara zai fi [maka].'" [Ya ce:] "Na ce: 'To kashi biyu cikin uku? 'Ya (SAW) ya ce: 'Yadda kake so, amma idan ka ƙara zai fi maka.' Na ce: 'Shin in sanya dukkan Salat ina a gare ka?' Ya (SAW) ya ce: 'A nan ne za a magance matsalolinka kuma a gafarta zunubanka.' Wannan hadisi yana gaya mana mu yawaita yin salati ga Annabi. Addu'o'in da suka tabbata daga Alƙur'ani da Sunnah ne kaɗai ya kamata a karanta dangane da wannan.
Reference: Sahih (Albani). Tirmidhi: 2457