Loading...
Language: Hausa
Ka hau kan dutsen Safa ka tsaya kana fuskantar Baitullah sannan ka bayyana egyen Allah, girmansa da yabon Allah -
لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيْكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ يُحْيِي وَيُمِيْتُ وَهَوُ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيْرٌ، لَا إِلَهَ إِلَّا اَللَّهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيْكَ لَهُ، أَنْجَزَ وَعْدَهُ، وَنَصَرَ عَبْدَهُ، وَهَزَمَ الْأَحْزَابَ وَحْدَةُ.
laa ilaaha illallaahu wahdahu laa sharika lahu, lahul mulku wa lahul hamdu yuh-i wa yumitu wa huwa ‘alaa kulli shayin qadir, laa ilaaha illallaahu wahdahu laa sharika lahu, anjaza wa’dahu wa nasara ‘abdahu, wa hazamal ahzaaba wa-’adah.
Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya. Mulki nasa ne. Yabo ya tabbata a gare Shi. Shi ne Yake bayar da rayuwa kuma Yake kashewa. Kuma Shi Mai iko ne a kan komai. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya. Ya cika alƙawarinSa, Ya taimaki bawanSa, kuma Shi kaɗai Ya karya ƙungiyoyin (maƙiya).
Reference: Sahih. Ibn Majah: 2512