Loading...
Language: Hausa
اَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ بِأَنَّ لَكَ الْحَمْدُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ الْمَنَّانُ بَدِيْعُ السَّمَوَاتِ وَالْأَرْضِ يَا ذَا الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ يَا حَيُّ يَا قَيُّومُ إِنِّي أَسْأَلُكَ
Allaahumma inni as'aluka bi-anna lakal-hamdu, laa ilaaha illaa antal-mannaanu badi'us-samawaati wal-ardi, yaa dhal-jalaali wal-ikram! Yaa ‘hayyu yaa qayyum! Inni as'aluka
Ya Allah, lallai ina roƙonKa domin dukkan yabo ya tabbata gare Ka, babu abin bautawa da gaskiya sai Kai, Mai Kyauta, Mai haliccar sammai da ƙasa, Ya Ma'abocin girma da ɗaukaka! Ya Rayayye Ya Mai tsayuwa da Kansa! Ina roƙonKa. An ruwaito cewa Anas bn Malik (RA) ya ce: "Ina zaune tare da Manzon Allah (SAW) sai ga wani mutum yana tsaye yana sallah... ya yi addu'a, kuma a cikin addu'arsa ya ce: (An ambaci addu'ar a sama) Sannan Annabi (SAW) ya ce: 'Shin kun san da me ya yi addu'a?' Suka ce: "Allah (SWT) da ManzonSa ne suka fi sani. Ya (SAW) ya ce: 'Na rantse da Wanda raina yake a hannunSa, ya roƙi Allah da SunanSa Mafi Girma, wanda idan aka kira Shi da shi, Yana amsawa, kuma idan aka roƙe Shi da shi, Yana bayarwa.'
Reference: Sahih (Albani). An-Nasai: 1300